Majalissar zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da fitar da kudi sama da naira miliyan 194 domin gudanar da karin ayyukan magance zaizayar kasa da ambaliyar ruwa a wajen da ake gina sabon asibitin kwararru na Kazaure.
Kwamishinan yada labarai matasa da wasanni na jiha Alhaji Bala Ibrahim Mamsa ya sanar da hakan bayan zaman majalisar da Gwamna Muhammad Badaru Abubakar ya jagoranta.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Ibrahim Mamsa yayi bayanin cewa majalisar ta amince da karin ayyukan ne sakamakon rahotan data samu wanda ke nuni da cewar zaizayar kasa da ambaliyar ruwa na barazana ga aikin gina asibitin.
Kwamishinan ya cigaba da cewa tun farko an bada kwangilar aikin ne akan kudi naira biliyan dubu 1 da miliyan 893.