Gwamnatin Tarayya za ta kirkiri ayyuka kimanin miliyan 10 a bangaren aikin gona, karkashin shirin samar da abinci da ayyukan yi.
Ministan aikin gona da raya karkara, Sabo Muhammad Nanono, ya sanar da haka a Abuja a wajen taron manema labarai na ministoci, gabannin bikin ranar abinci ta duniya.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Ana gudanar da bikin ranar abinci ta duniya a ranar 16 ga watan Oktoban kowace shekara a kasashe sama da 150 a fadin duniya domin wayar da kai da fadakar da mutane dangane da batun fatara da yunwa.
Minstan yace shirin samar da abinci da ayyukan yi, wani tsagi ne na shirin dorewar tattalin arzikin Najeriya na shugaban kasa Muhammadu Buhari, an kaddamar da shi a watan Yuli domin kara yawan filayen da ake nomawa a kowace jiha tare da bayar da bashin da babu kudin ruwa ga manoma, da sauransu.