Mutumin da ya samar da jaridar Democrat kuma tsohon shugaban kungiyar masu gidajen jarida na kasa, Mallam Ismaila Isa Funtua, ya rasu.
Ya mutu sanadiyyar bugun zuciya jiya Litinin da dare. Marigaryin ya rasu yana da shekaru saba’in da shida a duniya.
Babban mai taimakawa shugaban kasa akan kafafen yada labarai da hulda da jama’a, Mallam Garba Shehu, a cikin wata sanarwa yace shugaban kasa Muhammadu Buhari ya shiga matsananciyar damuwa da samun labarin mutuwar abokin tafiyarsa a siyasance, Isa Funtua.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Ana kyautata zaton cewa Isa Funtua na daya daga cikin masu karfin fada aji a gwamnatin Buhari.
Ance Isa Funtua tare da tsohon shugaban ma’aikatan shugaban kasa Abba Kyari da dan yayan shugaban kasa, Mamma Daura, sune wadanda suka fi kowa karfin iko a gwamnatin Buhari.