Kungiyyar cigaban masarautar Hadejia (HEDA) ta dora alhakin ambaliyyar ruwan da ke faruwa akan gwamnatocin yanzu da na baya na tarayya da jiha.
Masarautar dake yankin arewa maso gabas na jihar Jigawa, tana da kananan hukumomi 8 a karkashinta, wadanda suka hada da Hadejia, Kaugama, Auyo, Malammadori, Birniwa, Guri, Kirikasamma and Kafin Hausa.
Shugaban kungiyyar , Abdullah Sarki Kafinta, wanda ya zanta da manema labarai anan cikin garin Hadejia, ya bayyana takaicin sa kan yadda al’ummar cikin garin Hadejia suka rasa kadarorinsu, gidaje da rayukansu sanadiyyar ambaliyyar ruwan.
- An kara kama masu alaka da zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a jami’ar Texas
- Gwamnan jihar Zamfara ya yi alkawarin tsai da kudurin magance ma’aikatan da ke karbar albashi da yawa a jihar
- Kifewar jirgin ruwa yayi sanadiyyar mutuwar wasu dalibai 2 a jihar Kano
- Tinubu ya nuna rashin jindadinsa kan mafi karacin albashi na Naira 615,000
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
Sannan yayi kira ga gwamnatin tarayya da taimakawa al’ummar yankin da irin shuka daban daban da irin kifi daza a zuba a kududdufai idan ambaliyyar ruwan ta wuce.