Kungiyyar cigaban masarautar Hadejia (HEDA) ta dora alhakin ambaliyyar ruwan da ke faruwa akan gwamnatocin yanzu da na baya na tarayya da jiha.
Masarautar dake yankin arewa maso gabas na jihar Jigawa, tana da kananan hukumomi 8 a karkashinta, wadanda suka hada da Hadejia, Kaugama, Auyo, Malammadori, Birniwa, Guri, Kirikasamma and Kafin Hausa.
Shugaban kungiyyar , Abdullah Sarki Kafinta, wanda ya zanta da manema labarai anan cikin garin Hadejia, ya bayyana takaicin sa kan yadda al’ummar cikin garin Hadejia suka rasa kadarorinsu, gidaje da rayukansu sanadiyyar ambaliyyar ruwan.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sannan yayi kira ga gwamnatin tarayya da taimakawa al’ummar yankin da irin shuka daban daban da irin kifi daza a zuba a kududdufai idan ambaliyyar ruwan ta wuce.