Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa bisa rasuwar tsohon shugaban Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano Farfesa Abdulhameed Isa Dutse.
Marigarayin ya yiwa gwamnatin jihar Jigawa aiki tsakanin watan Fabrairun 1992 zuwa Fabrairun 1994 a matsayin kwamishinan lafiya, daga baya kuma ya zama sakataren gwamnatin jiha a karkashin mulkin tsohon gwamna Ali Sa’adu Birninkudu.
Shugaban kasar ya bayyana rasuwar marigayi a matsayin babban rashi ga fannin kiwon lafiya.
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
- An shawarci al’ummar jihar Jigawa su tashi tsaye wajen dasa bishiyoyi da renon su
- Ministan ma’aikatar albarkatun ruwa da tsaftar muhalli ya kaddamar da cibiyar samar da ruwan sha dake garin Birnin Kudu
- Gwamnatin tarayya ta bayyana shirinta na sake duba farashin lasisin hakar ma’adanai
- Sauye-sauyen tattalin arzikin da shugaba Bola Tinubu yayi ne ya fardado da Najeriya daga durkushewa
A sanarwar da Mallam Garba Shehu ya bayar a madadin shugaban kasa ta bayyana cewar rasuwar marigayi ta haifar da gibi ga yan Nigeria wajen cigaba da amfana da kwararrun likitocinta da suka sadaukar da rayuwarsu wajen bautawa al’umma.
Shugaba Buhari ya mika ta’aziyyarsa ga Asibitin Aminu Kano da Gwamnatin Jihar Jigawa da kungiyar likitoci bisa rasuwar kwararren likitan tare da adduar Allah Ya jikansa kuma saka shi a gidan Aljanna.