Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa bisa rasuwar tsohon shugaban Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano Farfesa Abdulhameed Isa Dutse.
Marigarayin ya yiwa gwamnatin jihar Jigawa aiki tsakanin watan Fabrairun 1992 zuwa Fabrairun 1994 a matsayin kwamishinan lafiya, daga baya kuma ya zama sakataren gwamnatin jiha a karkashin mulkin tsohon gwamna Ali Sa’adu Birninkudu.

Shugaban kasar ya bayyana rasuwar marigayi a matsayin babban rashi ga fannin kiwon lafiya.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
A sanarwar da Mallam Garba Shehu ya bayar a madadin shugaban kasa ta bayyana cewar rasuwar marigayi ta haifar da gibi ga yan Nigeria wajen cigaba da amfana da kwararrun likitocinta da suka sadaukar da rayuwarsu wajen bautawa al’umma.
Shugaba Buhari ya mika ta’aziyyarsa ga Asibitin Aminu Kano da Gwamnatin Jihar Jigawa da kungiyar likitoci bisa rasuwar kwararren likitan tare da adduar Allah Ya jikansa kuma saka shi a gidan Aljanna.