Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa bisa rasuwar tsohon shugaban Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano Farfesa Abdulhameed Isa Dutse.
Marigarayin ya yiwa gwamnatin jihar Jigawa aiki tsakanin watan Fabrairun 1992 zuwa Fabrairun 1994 a matsayin kwamishinan lafiya, daga baya kuma ya zama sakataren gwamnatin jiha a karkashin mulkin tsohon gwamna Ali Sa’adu Birninkudu.

Shugaban kasar ya bayyana rasuwar marigayi a matsayin babban rashi ga fannin kiwon lafiya.
- An miƙa wa hukumar INEC ƙorafin yi wa Sanata Natasha kiranye
- An kama masu zanga-zanga 1,133 a Turkiyya cikin kwana biyar
- Ba lallai ba ne haɗakar ƴan siyasar Najeriya ta yi tasiri – Shekarau
- Fursunoni 12 sun tsere daga gidan yari a jihar Kogi
- An kama mutum 12 bisa zargin kashe wani matashi a masallaci a jihar Kaduna
A sanarwar da Mallam Garba Shehu ya bayar a madadin shugaban kasa ta bayyana cewar rasuwar marigayi ta haifar da gibi ga yan Nigeria wajen cigaba da amfana da kwararrun likitocinta da suka sadaukar da rayuwarsu wajen bautawa al’umma.
Shugaba Buhari ya mika ta’aziyyarsa ga Asibitin Aminu Kano da Gwamnatin Jihar Jigawa da kungiyar likitoci bisa rasuwar kwararren likitan tare da adduar Allah Ya jikansa kuma saka shi a gidan Aljanna.