Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana alhininsa bisa rasuwar tsohon shugaban Asibitin Koyarwa na Mallam Aminu Kano Farfesa Abdulhameed Isa Dutse.
Marigarayin ya yiwa gwamnatin jihar Jigawa aiki tsakanin watan Fabrairun 1992 zuwa Fabrairun 1994 a matsayin kwamishinan lafiya, daga baya kuma ya zama sakataren gwamnatin jiha a karkashin mulkin tsohon gwamna Ali Sa’adu Birninkudu.

Shugaban kasar ya bayyana rasuwar marigayi a matsayin babban rashi ga fannin kiwon lafiya.
- Ƴansanda sun kama mutum mai shekara 60 kan zargin yi wa yarinya fyade a Bauchi
- An daure ‘yar Najeriya shekaru 70 a Amurka kan badakalar tallafin yara
- Mayaƙan Lakurawa sun kashe jami’an kwastam biyu a Kebbi
- Tinubu Ya Amince Najeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taron Shugabannin Hukumomin Ƙwallon Ƙafa Na Afirka
- Kwastam Da NDLEA Sun Kama Tabar Wiwi Ta Naira Biliyan 16.6 Da Aka Yi Fasa Kwaurinta Zuwa Najeriya
A sanarwar da Mallam Garba Shehu ya bayar a madadin shugaban kasa ta bayyana cewar rasuwar marigayi ta haifar da gibi ga yan Nigeria wajen cigaba da amfana da kwararrun likitocinta da suka sadaukar da rayuwarsu wajen bautawa al’umma.
Shugaba Buhari ya mika ta’aziyyarsa ga Asibitin Aminu Kano da Gwamnatin Jihar Jigawa da kungiyar likitoci bisa rasuwar kwararren likitan tare da adduar Allah Ya jikansa kuma saka shi a gidan Aljanna.