Hukumar yan sanda ta kasa ta zata hada hannu da kwamatin kasa da kasa na hukumar agaji ta Red Cross da sauran hukumomin cigaba, wajen bayar da horo ga sabuwar rundunar SWAT da ta maye gurbin rundunar yan sanda ta musamman dake yaki da ayyukan fashi da makami wato SARS.
Kusan jami’ai 1,850 ne ake sa ran zasu halarci shirin bayar da horon na tsawon makonni 3, wanda za’a gudanar a makarantar baiwa yan sanda horo dake Ila Oragun a jihar Osun, da kuma ta Ende Hills dake jihar Nassarawa.
Kakakin hukumar Frank Mba, yace jami’an sabuwar rundunar ta SWAT, zasu karbi horo ne kan dokokin kiyaye dan adam da hakkokinsa, makamar jami’in dan sanda a halin rikici, kamawa da kuma tsare mai laifi da dai makamantansu.
- Akwai yiwuwa a tilastawa ASUU shiga yajin aikin gama gari a fadin kasar nan
- Gwamnan jihar Kano ya kaddamar da rabon tallafin Naira 50,000 ga mata 4,800
- Za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa ƙasa mai tsarki domin sauke farali
- Wani matashi ya cinna wa masallaci wuta ana tsaka da Ibada
- Gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet kan ma’adinai da sauran albarkatun ƙasa
Masu gudanar da shirin bada horon sun hadar da jami’ai daga hukumomin cigaba, kwararru a fannin tsaro da kuma yan fafutuka daga kungiyoyn fararen hula.