Tsohon shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa, Farfesa Attahiru Jega da tsohon limamin katolika na Abuja, Cardinal John Onaiyekan, sun gayawa shugaban kasa Muhammadu Buhari cewa yan Najeriya na fuskantar manyan wahalhalu biyu na rashin tsaro da illar annobar corona.
A saboda haka suka yi kira ga shugaban kasa da yayi duk mai yiwuwa wajen magance rashin tsaro, ko da kuwa sai ya tsige shugabannin hukumomin tsaro.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sun sanar da haka cikin wata sanarwa dauke da sa hannun ‘ya’yan wata kungiya mai fafutukar zaman lafiya da mulki nagari.
Sun nemi shugaban kasa da ya assasa shirin tattaunawa domin magance tashe-tashen hankula daban-daban, wadanda suka hada da na kabilanci da addini.