Hukumar Jiragen Kasa ta Najeriya ta musanta rahotannin da ke zargin cewa mahara sun kai hari kan jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a shekaranjiya Litinin da rana.
Manajan Darakta na hukumar, Fidet Okiriya, wanda ya musanta hakan cikin wata sanarwa, yace rahotannin, kanzon kurege ne.
A cewarsa, akwai wasu bata gari wadanda suke yawan jefa manyan duwatsu kan jirgin kasa dake tafiya akan hanyar Abuja zuwa Kaduna.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sai dai, ya bukaci masu amfani da jiragen kasan da kada su razana, kasancewar ministan sufuri da hukumar jiragen kasa zasu tabbatar da tsaron lafiyar yan Najeriya akan hanyar.
Kazalika, manajan sufurin jiragen kasan Abuja zuwa Kaduna, Faskal Norli, ya tabbatar da cewa jirgin kasan ya isa tashar Idu a ranar Litinin kamar yadda aka tsara, kuma ya musanta duk wani hari daga mahara.