Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sahalewa kudirin samar da cibiyoyin binciken magunguna, da bada horo a kwalejojin karatun likita 6 dake shiyyoyin kasarnan.
Bugu da kari Shugaba Buhari, ya amince da karin kudin hukumar na shekarar 2020 zuwa naira biliyan 7 da miliyan 5, sabanin naira biliyan 3 da yake a baya.
Babban sakataren hukumar TETfund, Farfesa Sulaiman Bogoro, shine ya bayyana hakan, yayin taron kwamatin amintattu na shekarar 2020 da aka gudanar a Abuja.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Yace amincewa batun ya baiwa hukumar TETFund damar gina dakunan gwaje gwajen cutuka masu yaduwa biyu a kowacce shiyyar kasarnan, abinda zai sanya hukumar ta zama gagara misali, wajen samar da cibiyoyin gwajin cutar corona a Nigeria.
Farfesa Bogoro ya kuma ce kwamatin amintattun hukumar, ya amince da zuba naira miliyan 200, domin daukar nauyin wasu jami’o’i dama hukumar NAFDAC wajen gudanar da bincike kan cutar corona.