Gwamnatin tarayya ta amince da dawo da jigilar jiragen sama a cikin kasa da zarar komai ya daidaita, bisa tanadin ka’idojin kariya daga cutar corona na cikin gida da na kasa da kasa.
Shugaban kwamitin karta kwana na shugaban kasa kan cutar corona, Boss Mustapha, ya sanar da haka wajen taron manema labarai na kwamitin a Abuja.
Yace dawowa jigilar jiragen zata zo da karin kudin tikitin jirgin sama.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Yayi bayanin cewa karin kudin kayayyaki da na ayyuka, ba bangaren sufurin jiragen sama kadai ya shafa ba.
A cewarsa, farashin abubuwa sun yi tashin gwauron zabi tun bayan barkewar annobar.
An rufe filayen jiragen sama a Najeriya a watan Maris, lokacin da kasar ta fara kokarin dakile bazuwar cutar corona, wacce tayi silar mutuwar sama da mutane 500 a kasarnan.