Gwamnatin tarayya ta amince da dawo da jigilar jiragen sama a cikin kasa da zarar komai ya daidaita, bisa tanadin ka’idojin kariya daga cutar corona na cikin gida da na kasa da kasa.
Shugaban kwamitin karta kwana na shugaban kasa kan cutar corona, Boss Mustapha, ya sanar da haka wajen taron manema labarai na kwamitin a Abuja.
Yace dawowa jigilar jiragen zata zo da karin kudin tikitin jirgin sama.
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
- Karyewar gada ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 24 a lardin Guangdong na kudancin kasar China
- Isra’ila na dab da fara kai hare-hare birnin Rafah na kudancin Gaza ta ƙasa – Martin Griffiths
- Gwamnonin jahohin arewa sun bayyana damuwa bisa cigaba da karuwar rashin tsaro a shiyyar
- Gwamnatin Tarayya ta shirya tsaf domin bayar da cikakkiyar dama ga matatar man fetur ta Dangote
Yayi bayanin cewa karin kudin kayayyaki da na ayyuka, ba bangaren sufurin jiragen sama kadai ya shafa ba.
A cewarsa, farashin abubuwa sun yi tashin gwauron zabi tun bayan barkewar annobar.
An rufe filayen jiragen sama a Najeriya a watan Maris, lokacin da kasar ta fara kokarin dakile bazuwar cutar corona, wacce tayi silar mutuwar sama da mutane 500 a kasarnan.