Gwamnatin tarayya ta amince da dawo da jigilar jiragen sama a cikin kasa da zarar komai ya daidaita, bisa tanadin ka’idojin kariya daga cutar corona na cikin gida da na kasa da kasa.
Shugaban kwamitin karta kwana na shugaban kasa kan cutar corona, Boss Mustapha, ya sanar da haka wajen taron manema labarai na kwamitin a Abuja.
Yace dawowa jigilar jiragen zata zo da karin kudin tikitin jirgin sama.
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
- EFCC sun kai samame gidan tsohon gwamnan jihar Kogi Yahaya Bello da ke Abuja
- Kwamitin gudanarwa na jam’iyyar PDP a Najeriya ya bayyana goyon bayansa ga Umar Damagum
- MƊD za ta ƙaddamar da asusun neman taimako domin samar da kayan agaji ga Falasɗinawa a Gaza
- Gwamnan Jihar Jigawa ya nemi ma’aikatun jihar da su cimma yarjejjeniyar da jihar ta kulla da Ofishin FCDO
Yayi bayanin cewa karin kudin kayayyaki da na ayyuka, ba bangaren sufurin jiragen sama kadai ya shafa ba.
A cewarsa, farashin abubuwa sun yi tashin gwauron zabi tun bayan barkewar annobar.
An rufe filayen jiragen sama a Najeriya a watan Maris, lokacin da kasar ta fara kokarin dakile bazuwar cutar corona, wacce tayi silar mutuwar sama da mutane 500 a kasarnan.