Ministan aikin gona da raya karkara, Sabo Nanono, yace gwamnatin tarayya ta ware kudi naira biliyan 600 domin inganta baiwa manoma damar samun lamunin kudaden aikin gona a kasarnan.
Sabo Nanono yace kimanin manoma miliyan 2 da dubu 400 ake sa ran zasu amfana daga bashin wanda babu kudin ruwa a ciki, da aka tsara da nufin kara karfin gwiwar amfani da fasahar zamani wajen noman shinkafa da sauran amfanin gonar da ake sayarwa.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Ministan yayi jawabi a wajen kaddamar da shirin tallafawa noman shinkafa na daminar bana a kauyen Tofai dake yankin karamar hukumar Gabasawa ta jihar Kano.
Sabo Nanono yace shirin zai agazawa manoma wajen samun nasarar habaka yawan amfanin gona, da dogaro da kai da kuma yalwar abinci a kasa.