Ministan aikin gona da raya karkara, Sabo Nanono, yace gwamnatin tarayya ta ware kudi naira biliyan 600 domin inganta baiwa manoma damar samun lamunin kudaden aikin gona a kasarnan.
Sabo Nanono yace kimanin manoma miliyan 2 da dubu 400 ake sa ran zasu amfana daga bashin wanda babu kudin ruwa a ciki, da aka tsara da nufin kara karfin gwiwar amfani da fasahar zamani wajen noman shinkafa da sauran amfanin gonar da ake sayarwa.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Ministan yayi jawabi a wajen kaddamar da shirin tallafawa noman shinkafa na daminar bana a kauyen Tofai dake yankin karamar hukumar Gabasawa ta jihar Kano.
Sabo Nanono yace shirin zai agazawa manoma wajen samun nasarar habaka yawan amfanin gona, da dogaro da kai da kuma yalwar abinci a kasa.