Rundunar yansanda ta jihar Jigawa ta kama wasu matasa da ake zargin sun kware wajen satar babura a sakatariyar gwamnatin jiha dake Dutse.
A wata sanarwa da kakakin rundunar SP Abdu Jinjiri ya bayar, ta bayyana sunan mutanen da suka hada da Najib Salisu mazaunin Tarauni a Kano da Yusif Ibrahim mazaunin Dala a Kano da kuma Musa Nasiru dake zaune a Tudun Wada, Kaduna.
- Ronaldo ya yi alfahari da ɗansa ya buga wa Portugal tamaula
- Gwamna Uba Sani Ya Kafa Sabon Tarihi, Ya Yi Abin da ba a Taba Yi ba a Najeriya
- Tsohun gwamnan jihar Benue,ya baiyana cewa jam’iyyar PDP tana cikin mawuyacin hali da zai iya kai ta ga rushewa kafin 2027
- Sojoji masu mulkin Mali sun rusa dukkan jam’iyyun siyasa a kasar
- NiMET, ta fitar da sabon hasashen yanayi inda tace da yiwuwar ɓarkewar cututtukan ruwa a karshe shekara 2025
Mutanen uku da aka kama wadanda suke dauke da makulli na musamman da barayi ke anfani dashi wajen bude ababan hawa, sun ce suna satar babura daga wannan jiha zuwa wata, sannan kuma su sayar da baburan a kasuwanni.
Sanarwar ta kara da cewa mutanen 3n sun kuma tabbatar da cewa suna kokarin satar babur a sakatariyar gwamnatin jiha dake Dutse lokacin da aka kama su.
Yansanda na cigaba da gudanar da bincike dangane da lamarin.