Rundunar yansanda ta jihar Jigawa ta kama wasu matasa da ake zargin sun kware wajen satar babura a sakatariyar gwamnatin jiha dake Dutse.
A wata sanarwa da kakakin rundunar SP Abdu Jinjiri ya bayar, ta bayyana sunan mutanen da suka hada da Najib Salisu mazaunin Tarauni a Kano da Yusif Ibrahim mazaunin Dala a Kano da kuma Musa Nasiru dake zaune a Tudun Wada, Kaduna.
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
- Karyewar gada ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 24 a lardin Guangdong na kudancin kasar China
- Isra’ila na dab da fara kai hare-hare birnin Rafah na kudancin Gaza ta ƙasa – Martin Griffiths
- Gwamnonin jahohin arewa sun bayyana damuwa bisa cigaba da karuwar rashin tsaro a shiyyar
- Gwamnatin Tarayya ta shirya tsaf domin bayar da cikakkiyar dama ga matatar man fetur ta Dangote
Mutanen uku da aka kama wadanda suke dauke da makulli na musamman da barayi ke anfani dashi wajen bude ababan hawa, sun ce suna satar babura daga wannan jiha zuwa wata, sannan kuma su sayar da baburan a kasuwanni.
Sanarwar ta kara da cewa mutanen 3n sun kuma tabbatar da cewa suna kokarin satar babur a sakatariyar gwamnatin jiha dake Dutse lokacin da aka kama su.
Yansanda na cigaba da gudanar da bincike dangane da lamarin.