Fitaccen malamin addinin musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya gargadi gwamnatin tarayya da gwamnatocin jihoshi dangane da haramta tsarin karatun Almajiranci.
Malamin ya ayyana cewa Almajirai suna da ‘yancin gudanar da addininsu ba tare da wata tsangwama ba a kudin tsarin mulki.
Da yake jawabi a karshen taron ganawar malaman Tsangaya, Sheikh Dahiru Bauchi ya bukaci a kyale Almajirai su cigaba da karatunsu na Al’Qur’ani a karkashin malamansu.
- Akwai yiwuwa a tilastawa ASUU shiga yajin aikin gama gari a fadin kasar nan
- Gwamnan jihar Kano ya kaddamar da rabon tallafin Naira 50,000 ga mata 4,800
- Za’a fara jigilar maniyyata aikin hajjin bana zuwa ƙasa mai tsarki domin sauke farali
- Wani matashi ya cinna wa masallaci wuta ana tsaka da Ibada
- Gwamnatin tarayya ta ƙaddamar da shafin intanet kan ma’adinai da sauran albarkatun ƙasa
A cewarsa, hakane ya kamata saboda Almajirai kamar kowane dan Najeriya, suna da damar gudanar da addininsu da yancin zama duk inda suka ga dama a cikin kasa, kamar yadda aka tabbatar a kundin tsarin mulkin Najeriya na shekarar 1999.
Ya ayyana cewa malaman Tsangaya baza su lamunci a take musu hakki ba ta hanyar haramta tsarin Almajiranci, da kuma kwashe Almajirai daga gari zuwa wani gari.