Kwamishinan kare mahalli na jiha Alhaji Ibrahim Baba Chai-Chai ya sanar da hakan a lokacin da yake bayani kan bikin ranar mahalli da yaki da kwararowar hamada ta bana.
Yace za a raba dashen itatuwan ne ga al’umma kyauta domin dasawa a masallatai da gonaki da asibitoci da makarantu da kuma sauran wuraren taruwar jama’a.
- Gwamnatin Jigawa zata cigaba da tallafawa Jami’ar Fasaha ta gwamnatin tarayya dake garin Babura
- Aƙalla mutum 42 ne suka mutu sakamakon ƙyanda a jihar Adamawa
- Gwamnan Jihar Gombe ya yi kira ga sabbin zababbun shugabannin kananan hukumomi da su yi aiki tukuru
- Gwamna Dikko Radda ya kare ziyarar da gwamnonin Arewa suka kai kasar Amurka
- Kasar Turkiyya ta dakatar da duk wata hulɗar kasuwanci da Isra’ila
Baba Chai-Chai yayi kira ga jama’a da su marawa kudirin gwamnatin jihar baya na yaki da kwararowar hamada da zaizayar kasa.
A nasa bangaren, daraktan dazuka na ma’aikatar, Alhaji Haladu Bulama, yayi kira ga masu sarautun gargajiya da kungiyoyin sa kai da su hada kai da ma’aikatar wajen tabbatar da aiwatar da shirin kamar yadda ya kamata.