Kwamishinan kare mahalli na jiha Alhaji Ibrahim Baba Chai-Chai ya sanar da hakan a lokacin da yake bayani kan bikin ranar mahalli da yaki da kwararowar hamada ta bana.
Yace za a raba dashen itatuwan ne ga al’umma kyauta domin dasawa a masallatai da gonaki da asibitoci da makarantu da kuma sauran wuraren taruwar jama’a.
- Barcelona ta ba Lamine Yamal lamba 10
- An ɗaura auren Umaru Musa Yar’Adua Jnr., ɗan marigayi tsohon shugaban ƙasa, Alhaji Umaru Musa Yar’Adua, tare da amaryarsa Maryam Ayuba Shuaibu
- Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar (GCON), ya kawo karshen shakku da tsokaci, inda a hukumance ya fice dga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP),
- Manhajar TikTok ta goge fiye da bidiyo miliyan 3.6 a Najeriya saboda saba ka’idar dokokinta
- Tsohon Shugaban APC na ƙasa kuma tsohon Gwamnan Jihar Edo, ya fice daga jam’iyya APC zuwa jam’iyyar hadaka ta ADC
Baba Chai-Chai yayi kira ga jama’a da su marawa kudirin gwamnatin jihar baya na yaki da kwararowar hamada da zaizayar kasa.
A nasa bangaren, daraktan dazuka na ma’aikatar, Alhaji Haladu Bulama, yayi kira ga masu sarautun gargajiya da kungiyoyin sa kai da su hada kai da ma’aikatar wajen tabbatar da aiwatar da shirin kamar yadda ya kamata.