Kwamishinan kare mahalli na jiha Alhaji Ibrahim Baba Chai-Chai ya sanar da hakan a lokacin da yake bayani kan bikin ranar mahalli da yaki da kwararowar hamada ta bana.
Yace za a raba dashen itatuwan ne ga al’umma kyauta domin dasawa a masallatai da gonaki da asibitoci da makarantu da kuma sauran wuraren taruwar jama’a.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Baba Chai-Chai yayi kira ga jama’a da su marawa kudirin gwamnatin jihar baya na yaki da kwararowar hamada da zaizayar kasa.
A nasa bangaren, daraktan dazuka na ma’aikatar, Alhaji Haladu Bulama, yayi kira ga masu sarautun gargajiya da kungiyoyin sa kai da su hada kai da ma’aikatar wajen tabbatar da aiwatar da shirin kamar yadda ya kamata.