Kwamishinan kare mahalli na jiha Alhaji Ibrahim Baba Chai-Chai ya sanar da hakan a lokacin da yake bayani kan bikin ranar mahalli da yaki da kwararowar hamada ta bana.
Yace za a raba dashen itatuwan ne ga al’umma kyauta domin dasawa a masallatai da gonaki da asibitoci da makarantu da kuma sauran wuraren taruwar jama’a.
- Kananun yara 5 ne suka mutu sakamakon rashin iska a cikin motar da suka makale a jihar Neja
- Yan sanda a Jihar Kaduna sun kama wani babban mai sayar wa ’yan bindiga makamai
- ‘Yan bindiga da ke addabar al’umma sun ajiye makamansu bayan wata tattaunawar sulhu
- Bobrisky ya ɗaukaka ƙara domin ƙalubalantar hukuncin kotun da ta aike dashi gidan gyaran hali
- Kwamitin majalisar dattawa kan wutar lantarki ya gayyaci Ministan Lantarki na kasa
Baba Chai-Chai yayi kira ga jama’a da su marawa kudirin gwamnatin jihar baya na yaki da kwararowar hamada da zaizayar kasa.
A nasa bangaren, daraktan dazuka na ma’aikatar, Alhaji Haladu Bulama, yayi kira ga masu sarautun gargajiya da kungiyoyin sa kai da su hada kai da ma’aikatar wajen tabbatar da aiwatar da shirin kamar yadda ya kamata.