Ministan ayyuka, Babatunde Fashola, ya sanar da haka lokacin da yake gabatar da tsare-tsaren shirin ga hadakar kwamitocin ayyuka na majalisun kasa.
Ministan yace masu zuba jari zasu gudanar da aiki da kula da manyan titunan.
- Gwamna Otu Ya Fadi Abubuwan da ke Janye Gwamnoni zuwa jam’iyar APC
- Atiku Abubakar yayi magana kan ficewar sa daga PDP
- Hukumar NEMA ta karɓi ‘yan Najeriya 203 da aka kwaso daga kasar Libya
- Kwamiti na jam’iyyar PDP ta yanke shawarar daukar matakin shari’a kan Sheriff Oborevwori
- Hukumar NDLEA ta yi nasarar kama kwayoyin da kudinsu ya haura naira biliyan 2.6 a Jihar Jigawa
- Gwamnatin Jigawa za ta tantance yan fasho dake karkashin tsarin adashen gata a jihar
Fashola yace Zangon farko na aiki zai lakume kudi naira biliyan 163 da miliyan 320, akan kimanin naira biliyan 16 domin kowane titi guda daga cikin goman.
Titunan sune na Benin zuwa Asaba, Abuja zuwa Lokoja, da Kaduna
zuwa Kano, da Onitsa zuwa Owerri zuwa Aba, da Shagamu zuwa Benin, da Abuja zuwa
Keffi zuwa Akwanga, da Kano zuwa Maiduguri, da Lokoja zuwa Benin, da Enugu zuwa
Fatakwal da kuma Ilorin zuwa Jebba.