Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU ta bayyana umarnin gwamnatin tarayya na dakatar da albashin wadanda basu shiga sabon tsarinta na hadakar biyan albashi da tattara bayanai IPPIS, a matsayin wata hanyar nakasasu domin tilasta musu shiga tsarin.
- Sarki Charles zai koma aiki makon gobe
- Amurka ta bayar da bayanin tallafin soji na $6Bn da ta bai wa Ukriane
- Japan za ta taimakawa ƙananan ma’aikata a Najeriya domin samar da shinkafa
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
Shugaban kungiyar reshen jami’ar fatakwal Dr. Austen Sado, yace ko da yake wasu cikin abokan aikinsa, basu sami albashinsu ba tun watan fabarairun da ya gabata, said ai hakan, ba zai sanya kungiyar yin na’am da tsarin ba. Da ake hira dashi ta wayar talho, Sado yace umarnin na gwamnatin tarayya dangane da dakatar da albashinsu, manuniya ne cewa, akwai wani abu da take boyewa.