Kungiyar malaman jami’o’i ta kasa ASUU ta bayyana umarnin gwamnatin tarayya na dakatar da albashin wadanda basu shiga sabon tsarinta na hadakar biyan albashi da tattara bayanai IPPIS, a matsayin wata hanyar nakasasu domin tilasta musu shiga tsarin.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Shugaban kungiyar reshen jami’ar fatakwal Dr. Austen Sado, yace ko da yake wasu cikin abokan aikinsa, basu sami albashinsu ba tun watan fabarairun da ya gabata, said ai hakan, ba zai sanya kungiyar yin na’am da tsarin ba. Da ake hira dashi ta wayar talho, Sado yace umarnin na gwamnatin tarayya dangane da dakatar da albashinsu, manuniya ne cewa, akwai wani abu da take boyewa.