Gwamnan babban bankin kasa CBN Mr. Godwin Emefiele, yace za’a dauki matakin fadada wasu ka’idoji da nufin shawo kan karayar tattalin arziki, kasancewar ka’idojin dake akwai a yanzu haka sun kuntata.
Ya bayyana hakan a matsayin tilas domin shawo kan durkushewar tattalin arziki da kuma karancin wadatuwar takardun kudade a hannun jama’a, matakin da kwamatin tsare tsaren kudade na bankin ya cimma a taron da ya gudanar makon jiya.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Emmefiele ya alakanta hakan da janye tallafin mai na baya bayannan, da ya haddasa hauhauwar farashinsa, da kuma kwaskwarima da da akayiwa kasuwar canjin kudi, wanda yace muddin ba’a dauki matakan da suka kamata ba, to babu shakka kalubaken karancin takardun kudaden zai tsaurara.