Gwamnan babban bankin kasa CBN Mr. Godwin Emefiele, yace za’a dauki matakin fadada wasu ka’idoji da nufin shawo kan karayar tattalin arziki, kasancewar ka’idojin dake akwai a yanzu haka sun kuntata.
Ya bayyana hakan a matsayin tilas domin shawo kan durkushewar tattalin arziki da kuma karancin wadatuwar takardun kudade a hannun jama’a, matakin da kwamatin tsare tsaren kudade na bankin ya cimma a taron da ya gudanar makon jiya.
- Ƴansanda sun kama mutum mai shekara 60 kan zargin yi wa yarinya fyade a Bauchi
- An daure ‘yar Najeriya shekaru 70 a Amurka kan badakalar tallafin yara
- Mayaƙan Lakurawa sun kashe jami’an kwastam biyu a Kebbi
- Tinubu Ya Amince Najeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taron Shugabannin Hukumomin Ƙwallon Ƙafa Na Afirka
- Kwastam Da NDLEA Sun Kama Tabar Wiwi Ta Naira Biliyan 16.6 Da Aka Yi Fasa Kwaurinta Zuwa Najeriya
Emmefiele ya alakanta hakan da janye tallafin mai na baya bayannan, da ya haddasa hauhauwar farashinsa, da kuma kwaskwarima da da akayiwa kasuwar canjin kudi, wanda yace muddin ba’a dauki matakan da suka kamata ba, to babu shakka kalubaken karancin takardun kudaden zai tsaurara.