Mutane goma sha shida aka bayar da rahoton sun mutu, yayin da daruruwan gidaje da gonaki suka salwanta a ambaliyar ruwa daban-daban da aka samu a yankunan kananan hukumomi bakwai na jihar Jigawa.
Sakataren zartarwa na hukumar agajin gaggawa ta jiha, Yusuf Sani Babura, ya sanar da haka yayin wata ganawa da manema labarai a Dutse.
Yace an samu ambaliyar ruwan sanadiyyar mamakon ruwan sama cikin makon da ya gabata.
Kananan hukumomin da lamarin ya shafa sun hada da Taura, da Jahun, da Babura, da Ringim, da Dutse, da Birnin-Kudu, da Miga, da Kafin-Hausa, da Auyo, da Gwaram, da Malam-Madori, da Birniwa da kuma Kaugama.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sani Babura yayi bayanin cewa mutane sun mutu yayin da gine-gine suka zube a lokacin da ake ruwan sama, kuma mutane da dama sun samu raunuka daban-daban.
Ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta kuma yi awon gaba da dubban gonaki, inda ta lalata amfanin gona.