Mutane goma sha shida aka bayar da rahoton sun mutu, yayin da daruruwan gidaje da gonaki suka salwanta a ambaliyar ruwa daban-daban da aka samu a yankunan kananan hukumomi bakwai na jihar Jigawa.
Sakataren zartarwa na hukumar agajin gaggawa ta jiha, Yusuf Sani Babura, ya sanar da haka yayin wata ganawa da manema labarai a Dutse.
Yace an samu ambaliyar ruwan sanadiyyar mamakon ruwan sama cikin makon da ya gabata.
Kananan hukumomin da lamarin ya shafa sun hada da Taura, da Jahun, da Babura, da Ringim, da Dutse, da Birnin-Kudu, da Miga, da Kafin-Hausa, da Auyo, da Gwaram, da Malam-Madori, da Birniwa da kuma Kaugama.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sani Babura yayi bayanin cewa mutane sun mutu yayin da gine-gine suka zube a lokacin da ake ruwan sama, kuma mutane da dama sun samu raunuka daban-daban.
Ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta kuma yi awon gaba da dubban gonaki, inda ta lalata amfanin gona.