Mutane goma sha shida aka bayar da rahoton sun mutu, yayin da daruruwan gidaje da gonaki suka salwanta a ambaliyar ruwa daban-daban da aka samu a yankunan kananan hukumomi bakwai na jihar Jigawa.
Sakataren zartarwa na hukumar agajin gaggawa ta jiha, Yusuf Sani Babura, ya sanar da haka yayin wata ganawa da manema labarai a Dutse.
Yace an samu ambaliyar ruwan sanadiyyar mamakon ruwan sama cikin makon da ya gabata.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2020/08/jigawa-flood-2-1.jpg?resize=860%2C484&ssl=1)
Kananan hukumomin da lamarin ya shafa sun hada da Taura, da Jahun, da Babura, da Ringim, da Dutse, da Birnin-Kudu, da Miga, da Kafin-Hausa, da Auyo, da Gwaram, da Malam-Madori, da Birniwa da kuma Kaugama.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Sani Babura yayi bayanin cewa mutane sun mutu yayin da gine-gine suka zube a lokacin da ake ruwan sama, kuma mutane da dama sun samu raunuka daban-daban.
Ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta kuma yi awon gaba da dubban gonaki, inda ta lalata amfanin gona.