Mutane goma sha shida aka bayar da rahoton sun mutu, yayin da daruruwan gidaje da gonaki suka salwanta a ambaliyar ruwa daban-daban da aka samu a yankunan kananan hukumomi bakwai na jihar Jigawa.
Sakataren zartarwa na hukumar agajin gaggawa ta jiha, Yusuf Sani Babura, ya sanar da haka yayin wata ganawa da manema labarai a Dutse.
Yace an samu ambaliyar ruwan sanadiyyar mamakon ruwan sama cikin makon da ya gabata.

Kananan hukumomin da lamarin ya shafa sun hada da Taura, da Jahun, da Babura, da Ringim, da Dutse, da Birnin-Kudu, da Miga, da Kafin-Hausa, da Auyo, da Gwaram, da Malam-Madori, da Birniwa da kuma Kaugama.
- Kotu ta ɗage shari’ar Nnamdi Kanu har sai baba ta gani
- Yan bindiga sun kai hari wani masallaci a garin Sabon Birni
- Kwamitin zakka na masarautar Hadejia ya kaddamar da rabon zakkar da aka tattara a kauyen Masassadi
- Ma’aikatan lantarki na Kaduna sun dakatar da yajin aiki
- NAFDAC ta buƙaci a riƙa yanke wa masu jabun magunguna hukuncin kisa
Sani Babura yayi bayanin cewa mutane sun mutu yayin da gine-gine suka zube a lokacin da ake ruwan sama, kuma mutane da dama sun samu raunuka daban-daban.
Ya kara da cewa ambaliyar ruwan ta kuma yi awon gaba da dubban gonaki, inda ta lalata amfanin gona.