Kwamishinan ilimi, Kimiyya da fasaha na jihar Jigawa, Dakta Lawan Yunusa Danzomo ya bukaci kwalejojin fasaha su bujuro da tsare-tsare na bai-daya domin tafikar da al’amuransu yadda ya kamata.
Kwamishinan ya yi wannan kiran ne lokacin kaddamar da kwamitin da zai tsara ka’idojin aikin ma’aikatan kwalejojin fasaha wanda aka gudanar a kwalejin fasaha ta jiha dake Dutse.

Wakilan kwamitin sun hadar da magarakardar kwalejin fasaha ta jiha dake Dutse da na kwalejin Binyaminu Usman dake Hadejia da na cibiyar fasahar sadarwa ta jiha dake Kazaure da kuma wasu ma’aikatan kwalejojin.
Yace an dorawa kwamitin alhakin yin kyakykyawan nazari kan dokokin aikin gwamnati tare da sauran dokokin da suka tanadi aiwatar da harkokin kwalejojin.
- Kudurin kara yawan kananan hukumomin Jihar Legas daga 20 zuwa 57 ya tsallake karatu na biyu a zauren Majalisar Wakilai
- Tinubu ya amince da yin sabbin nade-nade guda hudu
- Ban san ko zan tsaya takarar shugabancin kasa a shekarar 2027 ba – Atiku
- Tinubu ya taya Goodluck Jonathan murna kan lashe kyautar “Sunhak Peace Founders Award” na shekarar 2025
- Masu haƙar kabari sun koka kan ƙarancin alawus ɗin da ake ba su na ₦3,000 a wata
A jawabin da ya gabatar amadadin wakilan kwamitin magatakardar cibiyar fasahar sadarwa ta jiha dake Kazaure, Malam Sadisu Buhari ya godewa m’`aikatar bisa basu damar gudanar da wannan aikin, inda ya yi alkawarin zasu gudanar da aikin kamar yadda ya kamata.