Kwamishinan ilimi, Kimiyya da fasaha na jihar Jigawa, Dakta Lawan Yunusa Danzomo ya bukaci kwalejojin fasaha su bujuro da tsare-tsare na bai-daya domin tafikar da al’amuransu yadda ya kamata.
Kwamishinan ya yi wannan kiran ne lokacin kaddamar da kwamitin da zai tsara ka’idojin aikin ma’aikatan kwalejojin fasaha wanda aka gudanar a kwalejin fasaha ta jiha dake Dutse.
Wakilan kwamitin sun hadar da magarakardar kwalejin fasaha ta jiha dake Dutse da na kwalejin Binyaminu Usman dake Hadejia da na cibiyar fasahar sadarwa ta jiha dake Kazaure da kuma wasu ma’aikatan kwalejojin.
Yace an dorawa kwamitin alhakin yin kyakykyawan nazari kan dokokin aikin gwamnati tare da sauran dokokin da suka tanadi aiwatar da harkokin kwalejojin.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
A jawabin da ya gabatar amadadin wakilan kwamitin magatakardar cibiyar fasahar sadarwa ta jiha dake Kazaure, Malam Sadisu Buhari ya godewa m’`aikatar bisa basu damar gudanar da wannan aikin, inda ya yi alkawarin zasu gudanar da aikin kamar yadda ya kamata.