Kwamishinan ilimi, Kimiyya da fasaha na jihar Jigawa, Dakta Lawan Yunusa Danzomo ya bukaci kwalejojin fasaha su bujuro da tsare-tsare na bai-daya domin tafikar da al’amuransu yadda ya kamata.
Kwamishinan ya yi wannan kiran ne lokacin kaddamar da kwamitin da zai tsara ka’idojin aikin ma’aikatan kwalejojin fasaha wanda aka gudanar a kwalejin fasaha ta jiha dake Dutse.

Wakilan kwamitin sun hadar da magarakardar kwalejin fasaha ta jiha dake Dutse da na kwalejin Binyaminu Usman dake Hadejia da na cibiyar fasahar sadarwa ta jiha dake Kazaure da kuma wasu ma’aikatan kwalejojin.
Yace an dorawa kwamitin alhakin yin kyakykyawan nazari kan dokokin aikin gwamnati tare da sauran dokokin da suka tanadi aiwatar da harkokin kwalejojin.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
A jawabin da ya gabatar amadadin wakilan kwamitin magatakardar cibiyar fasahar sadarwa ta jiha dake Kazaure, Malam Sadisu Buhari ya godewa m’`aikatar bisa basu damar gudanar da wannan aikin, inda ya yi alkawarin zasu gudanar da aikin kamar yadda ya kamata.