Sufeto Janar na Yansanda, Mohammed Adamu, ya dakatar da bukatar cancanta domin wadanda ke neman shiga aikin dansanda a matsayin kurata.
Mohammed Adamu a wani umarni da ya bayar, yace babu wadanda za a hana dama a wajen daukar aikin, bisa la’akari da yanayin halittarsa ko shekarunsa ko matakin karatunsa.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Hukumar a halin yanzu tana aikin daukar kuratan yansanda dubu goma domin magance karancin yansanda, kuma tuni aka fara aikin tantance masu neman aikin daga jiya Litinin zuwa ranar goma sha shida ga watan gobe na Satumba.
Kamar yadda yazo a wata sanarwa da kakakin hukumar dansanda, Frank Mba, ya fitar, ana sa ran masu neman shiga aikin suzo da number shaidar zama dan kasa da takardun karatu na ainihi da kwafi bibiyu, da takardar shaidar zama dan karamar hukuma da ta haihuwa, wadanda aka shirya cikin fararen files guda biyu, tare da kananan hotuna na fasfo.