Hukumar bada agajin gaggawa ta jihar jigawa ta tabbatar da mutuwar akalla mutane 40 a fadin jiharnan inda tace dubbun mutane ne suka tserewa muhallinsu da asarar gonakinsu sanadiyyar iftila’in amballiyar ruwa.
Shugaban hukumar Sani Ya’u Babura wanda ya tabbatar da mutuwar mutanen, yace hukumar su ta kammala tattara duk wani bayanai da zata turawa jami’anta domin bayar da agajin gaggawa ga wadanda iftala’in ya afkawa.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sani Babura ya kara da cewa sunyi kokari sosai wajan tattara adadin mutanen da suka rasa rayukansu, gonakinsu da wadanda suka tserewa muhallinsu.
Ya kara da cewa baya ga haka, Gwamnatin jihar jigawa na bukatar taimakon hukumar bada agajin gaggawa ta kasa NEMA.