Sarkin musulman Najeriya, Alhaji Sa’ad Abubakar ya bayyana ranar juma’a 31 ga watan da muke ciki a matsayin ranar sallar idi babba, tare da bukatar al’ummar musulmi su gudanar da sallar Idin a masallatan juma’a ba’a wajajan da aka saba gudanar da sallar idi ba.
Alhaji Sa’ad Abubakar yayi wannan kiran ne cikin sanarwar da shugaban kwamitin al’amuran addini, Sambo Junaidu ya fitar, a yayin ganawa da sarkin musulman yayi da yan Jaridu a jiya Alhamis a Sakkwato.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Sarkin musulmin yayi fatan kiyayewar ubangiji da albarkar sa ga al’ummar Najeriya baki daya.
Ya kuma bukaci al’ummar musulmai da su cigaba da addu’ar zaman lafiya, da kuma cigaba ga kasar Najeriya a yayin sakon sa na taya murnar sallah.