Sarkin musulman Najeriya, Alhaji Sa’ad Abubakar ya bayyana ranar juma’a 31 ga watan da muke ciki a matsayin ranar sallar idi babba, tare da bukatar al’ummar musulmi su gudanar da sallar Idin a masallatan juma’a ba’a wajajan da aka saba gudanar da sallar idi ba.
Alhaji Sa’ad Abubakar yayi wannan kiran ne cikin sanarwar da shugaban kwamitin al’amuran addini, Sambo Junaidu ya fitar, a yayin ganawa da sarkin musulman yayi da yan Jaridu a jiya Alhamis a Sakkwato.
- Gwamnatin Sokoto Ta Bai Wa Sojojin Najeriya Gudummuwar Motocin Sulke 62
- Guguwar Iska Ta Kashe Mutane Uku, Ta Lalata Gidaje Da Ababen More Rayuwa A Yobe
- Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Takwas, Sun Kwato Makamai A Katsina
- Gwamnan Zamfara: Na Ƙi Biyan Kuɗin Fansa Naira Miliyan 300, Na Ce Su Kashe ‘Yan Uwana
- EFCC Ta Gurfanar da Bello Bodejo Kan Zargin Badaƙalar Kuɗi
Sarkin musulmin yayi fatan kiyayewar ubangiji da albarkar sa ga al’ummar Najeriya baki daya.
Ya kuma bukaci al’ummar musulmai da su cigaba da addu’ar zaman lafiya, da kuma cigaba ga kasar Najeriya a yayin sakon sa na taya murnar sallah.