Sarkin musulman Najeriya, Alhaji Sa’ad Abubakar ya bayyana ranar juma’a 31 ga watan da muke ciki a matsayin ranar sallar idi babba, tare da bukatar al’ummar musulmi su gudanar da sallar Idin a masallatan juma’a ba’a wajajan da aka saba gudanar da sallar idi ba.
Alhaji Sa’ad Abubakar yayi wannan kiran ne cikin sanarwar da shugaban kwamitin al’amuran addini, Sambo Junaidu ya fitar, a yayin ganawa da sarkin musulman yayi da yan Jaridu a jiya Alhamis a Sakkwato.
- Amurka ta ce jami’anta na ganawa da sojojin da ke mulki a Jamhuriyar Nijar
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
Sarkin musulmin yayi fatan kiyayewar ubangiji da albarkar sa ga al’ummar Najeriya baki daya.
Ya kuma bukaci al’ummar musulmai da su cigaba da addu’ar zaman lafiya, da kuma cigaba ga kasar Najeriya a yayin sakon sa na taya murnar sallah.