Sarkin musulman Najeriya, Alhaji Sa’ad Abubakar ya bayyana ranar juma’a 31 ga watan da muke ciki a matsayin ranar sallar idi babba, tare da bukatar al’ummar musulmi su gudanar da sallar Idin a masallatan juma’a ba’a wajajan da aka saba gudanar da sallar idi ba.
Alhaji Sa’ad Abubakar yayi wannan kiran ne cikin sanarwar da shugaban kwamitin al’amuran addini, Sambo Junaidu ya fitar, a yayin ganawa da sarkin musulman yayi da yan Jaridu a jiya Alhamis a Sakkwato.
- An miƙa wa hukumar INEC ƙorafin yi wa Sanata Natasha kiranye
- An kama masu zanga-zanga 1,133 a Turkiyya cikin kwana biyar
- Ba lallai ba ne haɗakar ƴan siyasar Najeriya ta yi tasiri – Shekarau
- Fursunoni 12 sun tsere daga gidan yari a jihar Kogi
- An kama mutum 12 bisa zargin kashe wani matashi a masallaci a jihar Kaduna
Sarkin musulmin yayi fatan kiyayewar ubangiji da albarkar sa ga al’ummar Najeriya baki daya.
Ya kuma bukaci al’ummar musulmai da su cigaba da addu’ar zaman lafiya, da kuma cigaba ga kasar Najeriya a yayin sakon sa na taya murnar sallah.