Guraren gyaran motoci a jihar Jigawa sun koka akan karancin ayyuka daga masu motoci

0 122

Hakan dai na faruwa ne yayin da farashin kayan gyaran motan ya ninka fiye da ninki biyu bayan cire tallafin man fetur wanda ba a taba ganin irinsa ba inda man ya tashi daga naira 200 zuwa naira 700.

A Dutse, babban birnin jihar Jigawa, masu motoci a yanzu suna amfani da motocin haya ne domin zirga-zirga saboda farashin man fetur ya karu sosai, wanda ya sa manyan tituna suka zama Fakai

Adamu Abubakar daya ne daga cikin masu sana’ar  anikancin mota a Dutse, ya ce yana da mata da ’ya’ya biyu amma abinci yana neman ya gagari iyalansa  saboda rashin samun aikin gyaran mota ya yi karanci. Adamu Abubakar ya ce kafin a cire tallafin suna samun ciniki sosai domin masu motoci a koda yaushe suna zuwa kawo musu gyara.

Leave a Reply

%d bloggers like this: