Gwamnatin jihar Niger ta bayar da sanarwar cewa Almajirai 64 da akayiwa gwaji ya nuna suna dauke da cutar COVID-19 a jihar, sun samu lafiya za’a kuma maida su zuwa ga iyayan su.
Kwamishinan lafiya da ayyukan asibitoci na jihar Dr Muhammad Makusidi shine ya bayyana haka a lokacin da yake amsa tambayoyi daga wajan yan Jaridu a Minna.
Ya bayyana cewa wadanda ba yan asalin jihar bane an mayar da su zuwa jihohin su na asali.
- Al’ummar Indiya sun fara kaɗa kuri’a a zaɓen da aka kasa gida bakwai cikin makonni shida
- Jami’an ‘yan sanda a Katsina sun dakile wani hari da aka kai garin Sabuwa dake jihar
- Rundunar sojin Najeriya ba za ta tsagaita ba wajen kawar da masu aikata miyagun laifuka
- Shugaba Bola Tinubu ya amince da wasu tsare-tsare guda uku don inganta fannin ilimi a kasar nan
- Gwamnatin jihar Nasarawa ta dakatar da duk wata Ƙungiyar ’yan banga a jihar
Dr Muhammad ya kara da cewa kawo yanzu mutane 1,778 aka yiwa gwaji cikin su an samu mutane 166 da suka kamu da cutar.
Gwamnan jihar Abubakar Sani Bello a yayin ganawa da kwamitin karta kwana kan cutar COVID-19 a jihar bisa jagorancin Ibrahim Matane, ya umarci dalibai da ma’aikata su cigaba da kasancewa a gida biyo bayan cigaba da rufe makarantu da ofisoshi, sakamakon karuwar bullar cutar a jihar.