Mukaddashin shugaban kasa Yemi Osinbanjo yace yan najeriya shirye suke da biyan kudin wutar lanyarki idan aka inganta tsarin bada wutar.
Osibanjo ya bayyana hakane a wani taron karawa juna sani da aka gudanar ta kafar internet, na ganin dorewar wutar lantarkin bayan shudewar annobar covid19 wanda Emmanuel Chapel ya shirya a jiya lahdi a babban birnin tarayya Abuja.
- Gwamnatin jihar Binuwai ta ce an kammala shirye-shiryen fara samar da nau’in barasa a jihar
- An fara rangadin tantance kananan hukumomin da suka shafe kusan shekaru 10 babu wutar lantarki
- Gwamnan jihar Kano ya rattaba hannu kan dokar tantance lafiyar mata kafin aure a jihar Kano
- ‘Yan bindiga sun yi awon gaba da wani manajan bankin TAJ reshen jihar Zamfara
- EFCC ta kama wasu ma’aikatan kamfanin chanji a babbar kasuwar Wuse Zone 4 dake Abuja
- EFCC na binciken wasu manyan jami’an tsaro 10 bisa zargin almundahanar kudi Naira Bilyan 7.5
Yace ba gaskiya bane cewa da ake yan najeriya basa san biyan kudin wuta, ya kara cewa yan kasar basa farin ciki tsawon shekaru ganin yadda ake gudanar da harkokin bada wutar.
Mataimakin shuganan kasar ya kuma yi magana bisa kasafin kudin shekarar 2020 a harkar lafiya.
Osibanjo yace kasafin kudin shekarar 2020 da aka ware a fannin lafiya shine mafi yawa da aka taba warewa shekaru biyar da suka wuce.