Akwai alamu sosai dake nuna cewa daliban jami’o’in gwamnati a kasarnan za su cigaba da zama a gida kasancewar kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta yi watsi da umarnin gwamnatin tarayya na cewa dukkan makarantu a kasarnan su koma bakin aiki a ranar Litinin mai zuwa.
Shugaban kungiyar ta ASUU na kasa, Farfesa Biodun Ogunyemi, a wata ganawa ta wayar tarho tare da manema labarai, yace gwamnatin tarayya bada gaske take ba dangane da tattaunawarta da kungiyar, inda ya kara da cewa lakcarori baza su koma aiki cikin yunwa ba.
- An yi bikin rantsar da Vladimir Putin a matsayin shugaban Rasha karo na biyar
- An ci gaba da ƙidayar kuri’u bayan kammala zaɓen shugaban kasa a jiya a ƙasar Chadi
- Gwamnan jihar Yobe ya jinjinawa sojojin Najeriya kan yadda suka fatattaki mayakan Boko Haram
- Jihar Borno ta yi asarar kusan kashi 53 cikin 100 na ma’aikatanta na kiwon lafiya sakamakon rikicin Boko Haram
- Najeriya za ta tsare kanta domin yaki da kasar Rasha
Biodun Ogunyemi musamman ya caccaki Babban Akawu na Tarayya, Ahmed Idris, saboda take umarnin da shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bashi na biyan malaman jami’o’i albashi.
Yayi tsokacin cewa yan Najeriya su shirya fuskantar dogon yajin aiki a jami’o’i, bisa la’akari da yadda gwamnati ke yiwa tattaunawa tsakaninsu rikon sakainar kashi.