Trump Ya Yi Barazanar Kai Wa Oman Hari Kan Rikicin Iran

Trump ya yi barazanar kai wa Oman hari kan rikicin Iran

Shugaban Amurka Donald Trump ya yi barazanar kai wa Oman hari idan ta kawo cikas ga tattaunawar Washington da Iran kan Mashigar Hormuz.

Trump ya yi barazanar ne a wata tattaunawa da tashar Fox News ranar Litinin, inda ya ce Amurka na da hanyar sadarwa kai tsaye da wasu jami’an Rundunar Juyin Juya Halin Iran (IRGC).

“Idan Oman ta kawo cikas, za mu far mata da harin bam,” in ji Trump.

Barazanar ta zo ne bayan Iran ta ce ta cimma matsaya da Oman kan wata hanyar da jiragen ruwa za su bi wajen ratsa Mashigar Hormuz.

Sai dai IRGC ta musanta cewa tana tattaunawa da Amurka kai tsaye.

Trump ya kuma ce ya kamata Iran ta “ɗaga farar tutar miƙa wuya”, yana mai cewa Tehran na fama da matsala sakamakon rikicin.

Game da Gaza, Trump ya ce bai kamata Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare ba, yana mai cewa Hamas ta amince da ajiye makamanta.

Ya kuma ce Amurka na da wata hanya ta daban ta tattaunawa da Hamas domin ganin ta ajiye makamanta.

A halin yanzu, sake buɗe Mashigar Hormuz na daga cikin manyan batutuwan da ake tattaunawa a tsakanin Amurka da Iran.

Comments (0)
Add Comment