Wani da Ake Zargi A Harin Bam Na Majalisar Dinkin Duniya da Aka Kai A Abuja, Ya Bayyana Yadda Ya Shiga Boko Haram

Wani daga cikin wadanda ake tuhuma a shari’ar harin bam na Majalisar Dinkin Duniya da aka kai a Abuja, ya bayyana yadda ya shiga kungiyar Boko Haram a gaban kotu.

Mohammed Bashir Saleh, wanda ake tuhuma, ya fadi hakan ne a wani bidiyo da DSS ta gabatar yayin zaman kotun tarayya a Abuja.

A cikin bidiyon, Saleh ya ce haduwarsa da Khalid Al-Barnawi a Bauchi ce ta sa shi shiga Boko Haram.

An kama Al-Barnawi ne a shekarar 2016, bayan kusan shekaru biyar da harin wanda ya kasance na farko da aka kai wa wata hukuma ta kasa da kasa a Najeriya.

Harin ya yi sanadiyyar mutuwar fiye da mutane 20 tare da jikkata sama da 70.

Alkalin kotun ya dage shari’ar zuwa ranar 2 ga Maris domin ci gaba da bincike da tambayoyi.

Comments (0)
Add Comment