Kungiyar Manoman Shinkafa ta Kasa reshen Jihar Jigawa, ta shigar da karar Manoma 300 a Kotu, saboda gaza biyan kudaden bashin da suka ara a wurin kungiyar da nufin yin Noma.
Shugaban Kungiyar na Jihar Jigawa Alhaji Adamu Haruna Maigoro Hadejia, shine ya bayyana hakan inda ya kara da cewa wasu Manoman sun fara dawowa da kudaden da suka karba na Bashin.
A cewarsa wanda sukaki su kawo kudaden da suka karba bashi a hannun Kungiyar yanzu haka suna dawowa dashi, saboda kotu da umarcesu.
Haka kuma ya ce kungiyar tana sane da sunayen mutane 500 da sukaki su dawowa da kudaden da suka karba.
- An yi bikin rantsar da Vladimir Putin a matsayin shugaban Rasha karo na biyar
- An ci gaba da ƙidayar kuri’u bayan kammala zaɓen shugaban kasa a jiya a ƙasar Chadi
- Gwamnan jihar Yobe ya jinjinawa sojojin Najeriya kan yadda suka fatattaki mayakan Boko Haram
- Jihar Borno ta yi asarar kusan kashi 53 cikin 100 na ma’aikatanta na kiwon lafiya sakamakon rikicin Boko Haram
- Najeriya za ta tsare kanta domin yaki da kasar Rasha
Kazalika ya ce kimanin manoma dubu 1,887 ne suka karbi kayan Noma wanda suka hada da Takin Zamani da Magani da kuma kuma Injin feshi.