Wani labari daga birnin Kano na nuni da cewa kungiyar Kano Pillars na shirin kammala yarjejeniyar daukar wani dan wasa dan asalin kasar Kamaru domin takawa kungiyar wasa a kaka mai kamawa.
Dan wasan mai suna Ngweni Ndasi ya kasance yana taka ledarsa ne a kungiyar CRA de Morocco, dake kasar Moroccan.
- An kara kama masu alaka da zanga-zangar goyon bayan Falasdinawa a jami’ar Texas
- Gwamnan jihar Zamfara ya yi alkawarin tsai da kudurin magance ma’aikatan da ke karbar albashi da yawa a jihar
- Kifewar jirgin ruwa yayi sanadiyyar mutuwar wasu dalibai 2 a jihar Kano
- Tinubu ya nuna rashin jindadinsa kan mafi karacin albashi na Naira 615,000
- Burkina Faso ta dakatar da wasu kafafen watsa labarai da dama na Ƙasashen Yamma har sai baba ta gani
Rahotanni sun bayyana cewa dan wasan ya iso jihar Kano ne tun a ranar Laraba kuma har ya kammala gwajin tabbatar da lafiyarsa a babban asibitin koyarwa na Abdullahi Wase Specialists Hospital, Kano, a yau Alhamis, har ma yayi atisayen farko da kungiyar a karamin filin wasa ga Dawakin Kudu.
Shugaban kungiyar Alhaji Surajo Shuaibu Yahaya, ya bayyana cewar ana kyautata zaton dan wasan zai rattaba kwantiragi da kungiyar a karshen makon nan.