Kano Pillars na shirin daukar dan wasan Kamaru daga Morocco

Wani labari daga birnin Kano na nuni da cewa kungiyar Kano Pillars na shirin kammala yarjejeniyar daukar wani dan wasa dan asalin kasar Kamaru domin takawa kungiyar wasa a kaka mai kamawa.

Dan wasan mai suna Ngweni Ndasi ya kasance yana taka ledarsa ne a kungiyar CRA de Morocco, dake kasar Moroccan.

Rahotanni sun bayyana cewa dan wasan ya iso jihar Kano ne tun a ranar Laraba kuma har ya kammala gwajin tabbatar da lafiyarsa a babban asibitin koyarwa na Abdullahi Wase Specialists Hospital, Kano, a yau Alhamis, har ma yayi atisayen farko da kungiyar a karamin filin wasa ga Dawakin Kudu.

Shugaban kungiyar Alhaji Surajo Shuaibu Yahaya, ya bayyana cewar ana kyautata zaton dan wasan zai rattaba kwantiragi da kungiyar a karshen makon nan.

CameroonKano PillarsNPFL
Comments (0)
Add Comment