Wani labari daga birnin Kano na nuni da cewa kungiyar Kano Pillars na shirin kammala yarjejeniyar daukar wani dan wasa dan asalin kasar Kamaru domin takawa kungiyar wasa a kaka mai kamawa.
Dan wasan mai suna Ngweni Ndasi ya kasance yana taka ledarsa ne a kungiyar CRA de Morocco, dake kasar Moroccan.
- Ronaldo ya yi alfahari da ɗansa ya buga wa Portugal tamaula
- Gwamna Uba Sani Ya Kafa Sabon Tarihi, Ya Yi Abin da ba a Taba Yi ba a Najeriya
- Tsohun gwamnan jihar Benue,ya baiyana cewa jam’iyyar PDP tana cikin mawuyacin hali da zai iya kai ta ga rushewa kafin 2027
- Sojoji masu mulkin Mali sun rusa dukkan jam’iyyun siyasa a kasar
- NiMET, ta fitar da sabon hasashen yanayi inda tace da yiwuwar ɓarkewar cututtukan ruwa a karshe shekara 2025
Rahotanni sun bayyana cewa dan wasan ya iso jihar Kano ne tun a ranar Laraba kuma har ya kammala gwajin tabbatar da lafiyarsa a babban asibitin koyarwa na Abdullahi Wase Specialists Hospital, Kano, a yau Alhamis, har ma yayi atisayen farko da kungiyar a karamin filin wasa ga Dawakin Kudu.
Shugaban kungiyar Alhaji Surajo Shuaibu Yahaya, ya bayyana cewar ana kyautata zaton dan wasan zai rattaba kwantiragi da kungiyar a karshen makon nan.