Fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na jihar Kano, Malam Ibrahim Khalil, ya bayyana cewa jin waƙa yana ƙara nutsuwa, imani, ƙwazo da kuma zaburar da mutane.
Malam Khalil ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a wajen maulidin Annabi Muhammad (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi) na gidan Sheikh Malam Nasidi Abubakar Goron Dutse dake unguwar Goron Dutse a cikin birnin Kano.
Malamin, wanda shi ne Shugaban Majalisar Malamai ta Jihar Kano, ya ce: “Shi yasa da idan ana aikin gayya a kan kirawo Shafi’u, wani babban mawaƙi na Kano, da shi da masu kaɗa masa ganga, ana kaɗawa ana gangi ana waƙa, a kawo kunu a sha.
- Tsananin zafi yasa an rufe daukacin makarantun dake kasar Sudan ta kudu
- An sake sassauta dokar hana zirga-zirgar babura masu kafa uku a wasu sassan jihar Adamawa
- Sanata Abdul’Aziz Yari ya bukaci al’ummar Musulmi da su yi amfani da lokacin Ramadan wajen yi wa Shugaba Bola Tinubu addu’a
- Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 14 a kauyen Dogon Noma-Ungwan Gamo
- Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaga da Magumeri da Gubio a majalisar wakilai ya raba kayan abinci ga iyalai 5,000
Wasu lokuta ma a afa wani abu– ka ji garau, to a lokacin kai bai waye ba a lokacin, sai a dama a cikin kunu su sha, ka gan shi yana ta tsalle, har da to haka ake yi.
“To wannan saboda ɗan Adam, shi yasa za ku ga a cikin Sahihul Bukhari, lokacin da aka zo ana yin Masallacin Annabi (tsira da amincin Allah su ƙara tabbata a gare shi), da lokacin da ake haƙa Ramin Gwalalo, to ana rera waƙa, to Annabi ba ya rera waƙa, amma su sahabbai suna rerawa”.