Hedikwatar Tsaro ta kasa ta sanar da cewa kimanin Yan bindiga 200 ne suka mutu, biyo bayan barin wutar da Rundunarsu da Operation Hadarin Daji suka kaddamar ta sama a maboyarsu na Jihohin Katsina da Zamfara, a yakin Arewa Maso Yamma.
Shugaban Sashen Yada Labarai na hukumar Major Janar John Enenche, shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Abuja.
Inda ya ce Dakarunsu sun kashe Yan Bindigar ne a maboyarsu ta Ibrahim Mai’Bai cikin karamar hukumar Jibia ta Jihar Katsina, da kuma kyauyen Kurmin Kura cikin karamar hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara.
- Sarki Charles zai koma aiki makon gobe
- Amurka ta bayar da bayanin tallafin soji na $6Bn da ta bai wa Ukriane
- Japan za ta taimakawa ƙananan ma’aikata a Najeriya domin samar da shinkafa
- Gwamnatin Jigawa ta jadadda kudirinta na daukar kwararan matakai na rage talauci a jihar
- An kama haramtattun nakiyoyi 6,240 a hanyar Yauri zuwa Jega da ke Jihar Kebbi
Haka kuma ya ce sun kaddamar da harin ne bayan samun bayanan sirri wanda ya ce nuni da cewa Yan bindigar suna kokarin kaddamar da hare-hare ne akan wasu Yankunan da suke karkashin kananan hukumomi.