Hedikwatar Tsaro ta kasa ta sanar da cewa kimanin Yan bindiga 200 ne suka mutu, biyo bayan barin wutar da Rundunarsu da Operation Hadarin Daji suka kaddamar ta sama a maboyarsu na Jihohin Katsina da Zamfara, a yakin Arewa Maso Yamma.
Shugaban Sashen Yada Labarai na hukumar Major Janar John Enenche, shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Abuja.
Inda ya ce Dakarunsu sun kashe Yan Bindigar ne a maboyarsu ta Ibrahim Mai’Bai cikin karamar hukumar Jibia ta Jihar Katsina, da kuma kyauyen Kurmin Kura cikin karamar hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Haka kuma ya ce sun kaddamar da harin ne bayan samun bayanan sirri wanda ya ce nuni da cewa Yan bindigar suna kokarin kaddamar da hare-hare ne akan wasu Yankunan da suke karkashin kananan hukumomi.