Hedikwatar Tsaro ta kasa ta sanar da cewa kimanin Yan bindiga 200 ne suka mutu, biyo bayan barin wutar da Rundunarsu da Operation Hadarin Daji suka kaddamar ta sama a maboyarsu na Jihohin Katsina da Zamfara, a yakin Arewa Maso Yamma.
Shugaban Sashen Yada Labarai na hukumar Major Janar John Enenche, shine ya bayyana haka cikin wata sanarwa da aka rabawa manema labarai a Abuja.
![](https://i0.wp.com/www.sawabafm.com/wp-content/uploads/2020/05/army-2.jpg?resize=1008%2C756&ssl=1)
Inda ya ce Dakarunsu sun kashe Yan Bindigar ne a maboyarsu ta Ibrahim Mai’Bai cikin karamar hukumar Jibia ta Jihar Katsina, da kuma kyauyen Kurmin Kura cikin karamar hukumar Zurmi ta Jihar Zamfara.
- Ina alfahari da samun dimbin goyon bayan da ake bukata domin zama ‘yartakara – Kamala Harris
- An bukaci mazauna jihar Jigawa da su kula da matakan kariya domin dakile ambaliyar ruwa
- Ƙasashe 58 sun goyi bayan Ngozi Okonjo-Iweala ta yi tazarce a Shugabar Kungiyar Cinikayya ta Duniya
- Kungiyar Kwadago ta yi gargadi kan yunkurin dakushe zanga-zangar da ake shirin yi a fadin kasar
- Gwamnatin Tarayya ta gabatar da buƙatar ƙarin Naira tiriliyan 6.2 akan kasafin kuɗin bana
Haka kuma ya ce sun kaddamar da harin ne bayan samun bayanan sirri wanda ya ce nuni da cewa Yan bindigar suna kokarin kaddamar da hare-hare ne akan wasu Yankunan da suke karkashin kananan hukumomi.