Gwamnan jihar Jigawa Muhammad Baduru Abubakar ya rantsar da sabon babban Khadin Jihar tare da karin wasu alƙalan manyan kotuna a fadar gwamnatin jihar a jiya.
Da yake magana a wurin taron da aka yi shi ba tare da cikowar jama’a ba saboda halin da ake ciki na bukatar karancin cunkoso da bayar da tazara, Gwamna Badaru bukaci sabbin masu Shari’ar da su ji tsoron Allah yayin da suke aiwatar da aikin su.
Kwamishinan Shari’a na jihar Dr. Musa Adamu Aliyu ne ya jagoranci rantsuwar sabbin alƙalan biyu da kuma babban Khadin.
- ‘Yan bindiga sun kashe babban limamin masallacin Juma’a na kauyen Keita
- Gobara ta ƙone motoci da rumfunan katako takwas da kuma kayan aikin kafinta ƙurmus
- Kwamitin Masallacin Dutse ya raba buhunan Shinkafa buhu 30,000 ga zawarawa da sauran marasa galihu
- Kwamandojin Boko Haram biyu sun mika wuya ga sojojin rundunar hadin gwiwa ta MNJTF
- Dan takarar jam’iyyar adawa Bassirou Diomaye Faye ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar Senegal
Alƙalan manyan kotunan su ne mai shari’a Musa Ubale da mai shari’a Husseina Aliyu Adamu sai kuma Khadi Muhammad Sani Salihu.
Taron rantsuwa ya samu halartar mataimakin gwamna Malam Umar Namadi da kakakin majalisar dokoki ta jihar Alhaji Adamu Abdulkadir Fanini.