Hukumar kula da yan gudun hijira ta kasa tare da babban bankin kasa CBN sun kaddamar da wani shirin bayar da horon sana’o’i ga yan gudun hijira dubu 350 wadanda rikici ya raba da muhallansu a yankin arewa maso gabas.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar a Maiduguri, kwamishinan tarayya na hukumar, Bashir Muhammad, yace shirin wani bangare ne na kokarin hukumar wajen dawo da rayuwa kamar yadda aka saba ga yan gudun hijira a Najeriya.
- Airtel ta dakatar da bayar da bashin kati da data a Najeriya
- ’Yan adawa ba su isa su razanar da ni ba – Tinubu
- Sojoji sun kama masu satar man fetur a Legas, sun kama mutum 14
- Talauci ya ragu daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto
- Bayan shekaru 12 da sace ɗaliban Chibok 272, har yanzu ba a san makomar 83 ba
Yace duk wanda zai ci gajiyar shirin, yana da damar zaben koyon sana’o’i sama da kala 50, da suka hada da aikin hannu da kasuwanci da noma da sauransu.
Bashir Muhammad yace wadanda suka shiga shirin za kuma a basu horo tare da jari domin dogaro da kawunansu.