Hukumar kula da yan gudun hijira ta kasa tare da babban bankin kasa CBN sun kaddamar da wani shirin bayar da horon sana’o’i ga yan gudun hijira dubu 350 wadanda rikici ya raba da muhallansu a yankin arewa maso gabas.
Da yake jawabi a wajen bikin kaddamarwar a Maiduguri, kwamishinan tarayya na hukumar, Bashir Muhammad, yace shirin wani bangare ne na kokarin hukumar wajen dawo da rayuwa kamar yadda aka saba ga yan gudun hijira a Najeriya.
- Tsananin zafi yasa an rufe daukacin makarantun dake kasar Sudan ta kudu
- An sake sassauta dokar hana zirga-zirgar babura masu kafa uku a wasu sassan jihar Adamawa
- Sanata Abdul’Aziz Yari ya bukaci al’ummar Musulmi da su yi amfani da lokacin Ramadan wajen yi wa Shugaba Bola Tinubu addu’a
- Wasu ‘yan bindiga sun yi garkuwa da mutane 14 a kauyen Dogon Noma-Ungwan Gamo
- Dan majalisa mai wakiltar mazabar Kaga da Magumeri da Gubio a majalisar wakilai ya raba kayan abinci ga iyalai 5,000
Yace duk wanda zai ci gajiyar shirin, yana da damar zaben koyon sana’o’i sama da kala 50, da suka hada da aikin hannu da kasuwanci da noma da sauransu.
Bashir Muhammad yace wadanda suka shiga shirin za kuma a basu horo tare da jari domin dogaro da kawunansu.