Wasu yanmata 4 sun nutse a kogi sun mutu a kauyen Kafin Doki Yamma dake yankin karamar hukumar Gwaram a nan jihar Jigawa.
Kakakin rundunar yan sandar jihar jigawa SP Abdu Jinjiri ne ya tabbatar da faruwar lamarin ga manema labarai a Dutse.
A cewarsa lamarin ya faru ne a safiyar jiya talata a lokacin da yaran suke kokarin tsallake kogin domin zuwa gona.
Ya kara da cewa yanmatan hudu da suka mutu sun hada Bilkisu Haruna mai shekara 17, Shamsiyya Nuhu yar shekara 13, da Maryam Danlami shekara 12 da kuma Marakisiyya Musa mai shekara 13 a duniya, dukkanin su yan asalin kauyen Kafin Doki ne dake mazabar Sara a karkashin karamar hukumar Gwaram.
- Gwamnatin jihar Jigawa ta fito da wani shiri na amfani da fasaha wajen koyo da koyarwa a jihar
- Kungiyar NULGE reshen karamar Hukumar Buji ta yabawa wakilin mazabar Buji a majalisar dokoki
- Aƙalla fursunoni 118 ne suka tsere daga gidan yarin Suleja
- Kasashen Afirka sun amince su yi magana da murya daya domin yaki da ta’addanci
- An tsare wani mataimakin ministan tsaron kasar Rasha bisa zargin karbar cin hanci
Abdu Jinjiri ya kara da cewa ansamu nasarar tsamo gawar uku daga cikin su, sannan ana ci gaba da neman daya gawar.
Kazalika ya kara da cewa likita ya tabbatar da mutuwar wadanda akayi nasarar samun gawar ta su.