ASUU Ta Ba Gwamnatin Gombe Wa’adin Kwana 14 Na Tsunduma Yajin Aiki

0 35

ASUU ta ba Gwamnatin Gombe wa’adin kwana 14 na tsunduma yajin aiki

Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Ƙasa (ASUU), reshen Jami’ar Jihar Gombe (GSU), ta bai wa gwamnatin jihar wa’adin kwanaki 14 ta biya mata buƙatunta ko kuma ta tsunduma yajin aiki na sai baba ta gani.

A cikin wata sanarwa da shugaban reshen ƙungiyar, Dakta Mustapha S. Shehu, da sakatarenta, Dakta Aliyu Usman Shelleng, suka sanya wa hannu, ASUU ta ce matakin ya biyo bayan rahoton ziyarar da Majalisar Zartarwa ta Ƙasa (NEC) ta kai wa reshen.

Ƙungiyar ta ce NEC ta umarci reshen da ya fara yajin aikin gama-gari ba tare da ƙayyade lokacin kawo ƙarshensa ba, idan gwamnatin jihar ta gaza magance matsalolin da take ƙorafi a kansu bayan cikar wa’adin shiga yajin aikin da zai fara ranar Talata, 25 ga Agusta, 2026.

Daga cikin buƙatun malaman akwai biyan bashin alawus ɗin Earned Academic Allowance (EAA) na shekarun 2021 zuwa 2024, da kuma bashin ƙarin albashin kashi 25 da kashi 35 cikin 100.

Haka kuma, ƙungiyar na neman aiwatar da mafi ƙarancin albashin naira 70,000 tare da biyan bashin mafi ƙarancin albashin naira 30,000.

ASUU ta kuma buƙaci cikakken aiwatar da yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Gwamnatin Tarayya da ƙungiyar a shekarar 2025.

Sauran buƙatun sun haɗa da ƙarin alawus na kula da ɗalibai masu karatun digiri na biyu, alawus na koyarwa a aikace, horon masana’antu da tafiye-tafiyen bincike, da kuma ƙarin alawus na nauyin aiki.

Aminiya ta ruwaito cewa, kimanin watanni uku da suka gabata, ƙungiyar ta roƙi gwamnatin jihar da ta biya basussukan da ake bin malaman domin kauce wa yajin aiki.

Sai dai Shehu ya ce duk ƙoƙarin shugabancin ƙungiyar na tattaunawa da gwamnati domin warware batutuwan da suka shafi basussukan malaman bai haifar da wani sakamako ba.

Ya ce hakan ne ya sa ƙungiyar ta ɗauki matakin bai wa gwamnatin wa’adin kwanaki 14 kafin fara yajin aikin.

Leave a Reply