Alƙawarin Atiku Na Dawo da Tallafin Mai Ya Jawo Muhawara A Jigawa

0 29

Alƙawarin Atiku na dawo da tallafin mai ya jawo muhawara a Jigawa

Wasu mazauna Jihar Jigawa sun yi maraba da alƙawarin tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar na dawo da tallafin man fetur idan aka zaɓe shi shugaban Najeriya a zaɓen 2027, yayin da wasu ke ganin cewa hakan na iya zama wani alƙawarin siyasa kawai.

Atiku ya bayyana cewa zai dawo da tallafin man fetur idan ya lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027, matakin da ya bambanta da matsayinsa a lokacin yaƙin neman zaɓen 2023, lokacin da ya goyi bayan cire tallafin.

A Jigawa, mazauna jihar sun ce cire tallafin man ya ƙara tsadar rayuwa, musamman ta fuskar sufuri da farashin kayan abinci.

Wani mazaunin Dutse, Mukhtar Kaugama, ya ce cire tallafin ya shafi kusan dukkanin sassan tattalin arzikin ƙasar, tare da ƙara wa talakawa wahala.

Ya ce idan Atiku ya yi nasarar dawo da tallafin, hakan na iya rage wa jama’a nauyin tsadar rayuwa.

“Cire tallafin yanzu ya shafi dukkanin ɓangarorin tattalin arziki. Talakawa suna shan wahala,” in ji shi.

Shi ma Aminu Yahaya ya ce, “Alƙawarin Atiku na iya zama abu mai kyau, musamman idan manufarsa ita ce rage tsadar rayuwa.”

Ya ce Atiku, kasancewarsa tsohon mataimakin shugaban ƙasa, yana iya fahimtar irin matsalolin tattalin arzikin da ƙasar ke ciki.

“Idan aka dawo da tallafin, yanayin tattalin arziki na iya sauƙaƙa, kuma jama’a za su yi farin ciki. Maganar tasa na iya zama ta yaƙin neman zaɓe, amma kuma tana iya zama abin da zai yiwu,” in ji shi.

Salisu Abubakar Jaudi ya ce, ya yi farin ciki da alƙawarin Atiku, yana mai cewa zai goyi bayan duk wani mataki da zai rage wa jama’a wahala idan Atiku ya samu damar cika alƙawarinsa.

Haka kuma, Muhammad Ɗanladi daga Ƙaramar Hukumar Ringim ya ce bai san irin shirin da Atiku yake da shi ba, amma idan zai iya dawo da tallafin man fetur, hakan zai faranta ran ’yan Najeriya.

“Idan zai iya dawo da tallafin, ’yan Najeriya za su yi farin ciki, domin cire tallafin man fetur shi ne abin da ke damu mu kullum,” in ji shi.

Ba cire tallafi ba ne kaɗai mafita — Malamin jami’a
Sai dai wani malamin jami’a a Jigawa ya yi gargaɗin cewa bai kamata a kalli batun tallafin man fetur a matsayin mafita ɗaya tilo ga matsalolin tattalin arzikin Najeriya ba.

Malam Muhammad Bello, Mataimakin Farfesa a fannin Kimiyyar Siyasa da Nazarin Tsaro a Jami’ar Tarayya da ke Dutse, ya ce batun tallafin man fetur ya daɗe yana addabar Najeriya, tun kafin gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta hau mulki.

Ya ce gwamnatocin baya, ciki har da gwamnatin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, sun yi ƙoƙarin rage ko cire tallafin a hankali.

Sai dai ya ce abin da ya fi sanya jama’a jin raɗaɗin matsalar a yanzu shi ne cikakken cire tallafin da Gwamnatin Tinubu ta yi.

Farfesa Bello ya kuma zargi tsarin tallafin da aka yi a baya da samar da wata kafa da wasu masu faɗa-a-ji ke cin moriyar tsarin ba bisa ƙa’ida ba.

Ya ce cire tallafin ya toshe wasu hanyoyin da waɗannan mutane ke samun moriya.

Zargin dabarar siyasa
Sai dai malamin ya bayyana sauya matsayar Atiku kan tallafin a matsayin abin da yake “zagaye”, yana mai cewa hakan na iya kasancewa wata dabarar siyasa domin samun goyon bayan jama’a a zaɓen 2027.

Ya ce ’yan siyasa ya kamata su gabatar wa jama’a da manufofi masu ɗorewa maimakon amfani da wahalhalun da jama’a ke ciki wajen neman kuri’a.

A cewarsa, matsalar tattalin arzikin Najeriya ba ta ta’allaƙa ne kawai kan cire tallafin man fetur ba, domin akwai wasu matsaloli masu zurfi da suka shafi tsarin tattalin arzikin ƙasar.

Malam Bello ya kuma ce rashin ingantaccen aikin matatun man Najeriya na daga cikin abubuwan da ke ƙara tsadar man fetur.

Ya ce Najeriya na da ɗanyen mai, amma ta shafe shekaru tana fitar da shi zuwa ƙasashen waje domin tacewa, sannan ta dawo da man da aka tace cikin ƙasar.

“Da matatun manmu suna aiki yadda ya kamata, batun sayen litar fetur kan N1,300 da an daina jin labarinsa,” in ji shi.

Ya ƙara da cewa ya kamata a bai wa sauye-sauyen tattalin arzikin da gwamnati ke aiwatarwa lokaci domin a ga sakamakonsu, musamman a fannin gine-ginen ababen more rayuwa da shirye-shiryen tallafa wa jama’a.

Gwamnati ta soki alƙawarin Atiku
A gefe guda kuma, Gwamnatin Tarayya ta yi kakkausar suka ga duk wani shiri na dawo da tallafin man fetur, tana mai cewa hakan na iya sake jefa kuɗaɗen gwamnati cikin matsala tare da kawo cikas ga sauye-sauyen tattalin arzikin da ake yi.

Gwamnati ta ce kuɗaɗen da aka samu sakamakon cire tallafin suna taimakawa wajen ƙara yawan kuɗaɗen da ake raba wa jihohi da ƙananan hukumomi, tare da gudanar da ayyukan raya ƙasa da shirye-shiryen tallafa wa al’umma.

Yayin da zaɓen 2027 ke ƙara kusantowa, batun tallafin man fetur na iya zama ɗaya daga cikin manyan batutuwan da za su mamaye muhawarar siyasa.

A Jigawa kuwa, ra’ayoyin jama’a sun nuna cewa akwai masu son a dawo da tallafin domin rage musu tsadar rayuwa, yayin da wasu ke ganin cewa ya kamata a nemo mafita mai ɗorewa da za ta magance tushen matsalar tattalin arzikin ƙasar.

Leave a Reply