

- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Mai Alfarma Sarkin Musulmai Kuma Shugaban Jama’atul Nasril Islam, Alhaji Muhammad Abubakar Sa’ad, yace babu taron lakca, wa’azi da tafsirin Ramadan a wannan shekara, saboda barkewar annobar corona.
Sarkin ya kuma ayyana cewa babu sallar jam’i a masallatai dake fadin kasarnan a wannan shekarar.
A wata sanarwa wacce sakataren Jama’atul Nasril Islam, Dr. Khalid Abubakar Aliyu ya fitar, Sarkin Musulman ya bukaci dukkan musulmai da suyi sallolinsu a gida, kasancewar baza su laminci ganganci da rayuwarsu ba.
Sarkin ya hori musulmai da su karanta Al-Qur’ani mai tsarki tare da sauraron lakcocin, wa’azozi da tafsiran watan Ramadan ta shafukan intanet da sauran hanyoyi.