Kenneth Okonkwo: Tinubu Ba Zai Lashe Zaɓen 2027 Ba

0 34

Kenneth Okonkwo: Tinubu Ba Zai Lashe Zaɓen 2027 Ba

Kakakin yaƙin neman zaɓe na ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar African Democratic Congress (ADC), Atiku Abubakar, Kenneth Okonkwo, ya bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu ba zai sake lashe zaɓen shugaban ƙasa na 2027 ba.

Okonkwo, wanda ya bayyana hakan a wata hira da Symfoni TV, ya ce bayan kammala zaɓen 2027, Tinubu zai bar mulki, yana mai cewa hanyar samun nasara a buɗe take ga Atiku Abubakar.

Tsohon jarumin fina-finan Nollywood da ya koma siyasa ya bayyana gwamnatin Tinubu a matsayin mafi muni a tarihin Najeriya, yana zargin cewa idan ba tare da magudin zaɓe ba, shugaban ƙasar ba zai iya lashe ko jiha ɗaya ba.

Ya ce a lokacin yaƙin neman zaɓen 2023, ADC ba ta da gwamna ko wata babbar madafa ta gwamnati, amma hakan bai hana Tinubu samun gagarumar nasara ba.

“Lokacin da muka yi yaƙin neman zaɓen 2023, ba mu da gwamna. Ba mu da komai, kuma Tinubu bai lashe jihohi da yawa fiye da mu ba.

“Yanzu da yake shi ne shugaban da ya fi kowa muni da Najeriya ta taɓa samu, kuna ganin zai iya lashe wata jiha ba tare da magudi ba? Tinubu ba zai lashe ko jiha ɗaya ba. Don haka hanyar samun nasara a buɗe take. Da yardar Allah, za mu yi nasara,” in ji Okonkwo.

Leave a Reply