Aikin samar da fasfo zai fara aiki daga ranar 8 ga Janairu, 2024

0 126

Ministan cikin gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya tabbatar da cewa aikin samar da fasfo zai fara aiki daga ranar 8 ga Janairu, 2024.

Ministan ya bayyana hakan a watan Disamba cewa gwamnatin tarayya na kokarin tabbatar da cikakken tsarin gudanar da aikin samar da fasfo a kasar nan.

Ya ce tsarin aikace-aikacen samar da fasfo ya samu kashi 99 cikin dari wanda ya hada da sanya hotunan fasfo da sauran muhimman takardu. Ojo ya tabbatar da cewa ‘yan Najeriya za su iya nema dayin rijistar neman fasfo din su ta yanar gizo ba tare da tuntubar wani mutum ba.

Leave a Reply

%d bloggers like this: