

Latest posts by Sawaba FM (see all)
- Anyi hasashen samun ruwan sama hade da tsawa a fadin kasarnan daga yau zuwa ranar Laraba - August 23, 2021
- Wata kungiyar adawa ta ce tana da dubban mayaka da zasu fafata yaki da yan Taliban a Afghanistan - August 23, 2021
- ‘Yan bindiga sun kashe mutane 4 tare da sace wasu 50 a karamar hukumar Maradun ta jihar Zamfara - August 23, 2021
Babban alkalin alakalai na jihar Jigawa Aminu Ringim ya kaddamar da kotun sauraron korafe korafen zaben kananan hukumomi da za’ayi a ranar 29 ga watan Yuni.
Da yake kaddamar da kotunan a Dutse ya bayyana cewa samar da kotunan na kunshe ne cikin dokar hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa INEC ta shekara 2012.
Ya bayyana cewa kotun korafe korafen tana da karfin sauraron karbar dukkanin wasu korafe korafen da suka shafi zabe batare da katsalandin wata kotu ba.
Mai shari’a Aminu Ringim ya ce kotun tana da ofis ofis a yankunan Dutse, Hadejia, da kuma Ringim.
Ya kuma ce shelkwatar kotun zata kasance a Dutse babban birnin Dutse.